Anyi ram da wasu direbobi wanda suke kasashen ketare da satar mai a Nigeria.
Nadaga cikin ma'aikatan manyan tankoki guda sha shida
Yan asalin kasashen waje angurfanar dasu agabar wata kotu dake jihar rivers a tarayyan Nigeria abisa zarginsu da hannu dumu dumu asafarar danyan mai a Nigeria ba bisa ka'ida ba.
RFI ta bayyanar cewa wannan sabon al-amari yazone adai-dai lokacin da Nigeria ke kokarin dakile yawan satar danyan mai daketa faruwa akasar, shine abin da ke janyo ma kasar asarar billiyoyin daloli.
Mahukunatan Nigeria sun zargi mutanen da dibar man agabar ruwan Akpo akan rashin bisa ka'ida tun awatan Augustan daya gabata sannan dakarun rundunar sojojin ruwan kasar suka kamasu dakuma tankar man.
Akarin jawabi da tayi rundunar sojin ruwan Nigeria an damke tankar man ne a equatorial Guinea Bayan Mahukunta kasar suka tsareta tareda sanar da jami'an Nigeria.
Wadanda ake zargin da dukkaninsu ma'aikatan jirgin ne sun musanta laifin da ake tuhumarsu da ita, sai dai aduk dahaka mai sharia Turaki Muhammad yabada umurnin tsaresu karkashin ikon rundunar sojin ruwan kafin atattaro kafin akaro wasu mutane goma (10)da'ake zarginsu tare.
Bayanai suntabbatar da cewa sun hadar da Yan asalin kasashen India, srilanka da Philippines.
0 Comments